in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi bikin tunawa da nasarar yaki da harin Japan na da ma'ana sosai a fannin kiyaye zaman lafiya, in ji jakadan Afghanistan dake Sin
2015-08-27 15:57:19 cri

Ranar 3 ga watan Satumba rana ce ta cika shekaru 70 da cimma nasarar yaki da harin Japan ta jama'ar kasar Sin, kuma kasar Sin za ta yi faretin soja da wasu jerin bukukuwan tunawa. Jakadan Afghanistan dake nan Sin Mohammad Kabir Farahi ya bayyana a kwanan baya a nan birnin Beijing cewa, kasar Sin ta yi bikin tunawa da nasarar yaki da harin Japan domin yin kira ga kasashen duniya da su darajanta da kuma kiyaye zaman lafiyar duniya.

Mohammad Kabir Farahi ya bayyana hakan ne a yayin da yake ganawa da wakilin CRI kafin bikin tunawa da za a yi a ranar 3 ga watan Satumba. Inda ya ce, kasar Sin ta ba da babbar gundummawa wajen yaki da harin Japan, lamarin da ya gaggauta wajen tabbatar da zaman lafiya a duniya.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China