in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kai farmakin boma-bomai a masallacin kasar Saudiyya
2015-08-07 11:25:38 cri

Kungiya mai tsattsauran ra'ayi ta IS ta sanar da daukar alhakin kai farmakin boma-boman kunar bakin wake a wani masallacin dake kudu maso yammacin kasar Saudiyya a jiya Alhamis, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 15, a yayin da mutane 7 suka ji rauni.

Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Saudiyya ta ce, a tsakar ranar Alhamis, an kai hari kan wani masallacin da ke karkashin wata rundunar 'yan sanda ta kasar Saudiyya, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar 'yan sanda 10 da kuma ma'aikata 3, a yayin da mutane 9 suka ji rauni, kuma 'yan sanda 2 daga cikinsu sun rasu a lokacin da suke karbar jinya.

Bayan fashewar boma-boman, kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kai wannan farmaki a kan shafinta na internet, tare da fayyace cewa, za ta kai kuma wasu karin hare-hare a kasashen Larabawa a nan gaba.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China