in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Rwanda ya yi allawadai da yammacin duniya kan tsare shugaban hukumar leken asirin kasarsa
2015-06-26 10:31:41 cri

Shugaban kasar Rwanda, Paul Kagame, ya soki kasashen yammacin duniya da tilasta nuna karfinsu da nuna isa da kai kan kasashen Afrika da ke kokarin sake gina kansu.

Korafe korafen shugaba Kagame sun biyo bayan cafke shugaban hukumar leken asirin kasarsa, mista Karenzi Karake a ranar Asabar, wadanda jami'an Burtaniya suka kama bisa doka.

Shugaban kasar Rwanda ya yi wannan furuci ne a yayin da yake jagorantar bikin rantsar da sabon mininistan ilimi, da wasu sabbin 'yan majalisu hudu da kuma sabbin alkalai, bikin da aka gudanar a zauren majalisar dokokin kasar ta Rwanda. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China