in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya nemi a kara yin yaki da shan miyagun kwayoyi
2015-06-25 21:06:21 cri

A jajibirin "ranar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa da kasa", a yau 25 ga wata da yamma a nan birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da wakilan hukumomi da kungiyoyin mutanen da ke yaki da fatauci da shan miyagun kwayoyi.

A yayin ganawar, Xi Jinping ya jaddada cewa, ta'ammali da miyagun kwayoyi yana shafar tsaron kasa, da makomar al'ummar kasa da kuma albarkar jama'a. Sabo da haka, daukar kwararan matakan yakar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi mataki ne da jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin da gwamnatin kasar Sin suke dauka a kullum. Dole ne hukumomi na yankuna daban daban na kasar su sa aikin yakar laifin miyagun kwayoyi tamkar wani nauyin siyasa da aka dora musu. Kuma ya kamata a ilmantar da jama'a, musamman yara da matasa game da yakar batun ta'ammali da miyagun kwayoyi. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China