in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mayakan Al-Shabaab sun halaka wani jami'i gwamnati a arewa maso gabashin Kenya
2015-06-22 13:18:48 cri

Wasu 'yan bindiga da ake zaton mayakan Al-Shabaab ne sun halaka wani jami'in gwamnatin kasar Kenya a garin Wajir da ke kan iyaka a arewa maso gabashin kasar.

Jami'in 'yan sandan yankin Wajir Samuel Mukindia ya tabbatar da cewa, wasu 'yan bindiga sun harbe Mohamed Barre Abdullahi har lahira a kan hanyarsa ta dawowa gida daga masallaci. Kuma har yanzu ba a kai ga gano wadanda suka aikata wannan danyen aiki da kuma manufarsu ba.

Kisan na baya-bayan nan na zuwa ne kwanaki uku kacal bayan da gwamnati ta dage dokar hana fita ta watanni biyu da aka sanya a shiyyar da ke iyaka da kasar Somaliya da yaki ya daidaita, a wani mataki na baiwa musulmi isasshen lokacin yin salar ashiyam da sauran Ibadu a watan Ramadan.

A baya ne dai gwamnati ta sanya dokar hana fita, sakamakon kashe wasu mutane 148 da mayakan Al-Shabaab suka yi ranar 2 ga watan Afrilu a jami'ar Garissa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China