in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban majalisar CPPCC ya gana da tawagar majalisar kula da tattalin arziki da zaman al'umma da kuma muhalli ta Senegal
2015-06-02 18:50:46 cri
A yau Talata 2 ga wata, shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta Sin (CPPCC), Yu Zhengsheng ya gana da tawagar majalisar kula da tattalin arziki da zaman al'umma da kuma muhalli ta Senegal bisa jagorancin shugabar majalisar, Aminata Tall a nan birnin Beijing.

Yu ya ce, Sin tana dora muhimmanci sosai kan bunkasa dangantaka tsakaninta da Senegal, kuma ta nuna mata goyon baya a kokarinta na raya manyan ayyuka masu amfanin jama'a, da raya tattalin arziki, da kyautata rayuwar jama'a. Majalisar CPPCC na fatan karfafa hadin gwiwa da sada zumunci tsakaninta da majalisar dokoki da sauran sassan kasar Senegal, tare da kara yin mu'amala da hadin gwiwa tsakaninta da majalisar kula da tattalin arziki, da zaman al'umma, da kuma muhallin kasar, ta yadda za a sa kaimi ga bunkasa dangantakar kasashen biyu zuwa wani sabon mataki.

A nata bangare kuma, madam Tall ta bayyana cewa, Senegal ta nuna yabo ga manufar da Sin take bi a fannin yin hadin gwiwa da kasashen Afirka, kuma tana fatan karfafa dangantakar abokantaka tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata, tare da zurfafa hadin gwiwa tsakaninsu a fannonin tattalin arziki, cinikayya, da kuma zuba jari.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China