A jiya Lahadi da karfe 6 na safe ne, jiragen ruwa na sojojin kasashen Sin da Rasha suka fara wani atisayen soja mai taken "hadin kai a teku na farko na shekarar 2015" inda sun isa yankin tekun Bahar Rum, don hade wa da juna a matsayin wata kungiya.
An fara yin atisayen soja mai taken "hadin kai a teku na farko na shekarar 2015"ne a ranar Litinin 11 ga wata da safe a birnin Novorossiysk na kasar Rasha. Za a fara atisayen soja a kan taswira ne daga ranar 11 zuwa 12 ga wannan wata, sannan a fara hade jiragen ruwa na kasashen biyu zuwa kungiya daga ranar 12 zuwa 17 ga wannan wata.(Lami)