in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Buhari ya ci zaben shugaban kasar Nijeriya
2015-04-01 14:57:40 cri

A sanyin safiyar yau Laraba, bisa sakamakon kidayar kuri'un babban zaben kasar Nijeriya da aka fidda, an sanar da dan takarar jam'iyyar APC Janar Muhammadu Buhari a matsayin zababben shugaban kasar da ya lashe zaben da aka yi tsakanin shi da dan takarar jam'iyyar PDP wato tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan.

Bayan da aka kammala jefa kuri'u a ranar Lahadi, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar INEC ta fara kidayar kuri'u a cibiyar taron kasa da kasa ta Abuja.Bisa sakamakon da aka samu, an ce, Muhammadu Buhari ya samu kuri'un da yawansu ya kai kashi 53.95 cikin dari, yayin da Jonathan ya samu kashi 44.96 cikin dari.

Wannan shi ne karo na farko, da jam'iyyar PDP ta fadi babban zabe cikin shekaru 16 da ta kafa gwamnati, wanda ta samu shugabannin kasar da suka hada da Olusegun obasanjo, marigayi Umaru Musa Yar 'Adua da kuma Goodluck Jonathan.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China