in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar zaben Najeriya ta dage zaben 'yan majalisar wakilai a jihar Jigawa
2015-03-28 15:41:29 cri
Hukumar zaben Najeriya ta dage zaben 'yan majalissar wakilai a dukkan mazabun jihar Jigawa 11.

Kwamishinan hukumar INEC a jihar ta Jigawa Alhaji Halliru Aliyu ne ya tabbatar da hakan ga manema labaru a birnin Dutse, fadar gwamnatin jihar.

Aliyu ya ce hakan ya biyo bayan matsalar karancin kayan aikin gudanar zaben da aka ci karo da ita ne. Sai dai ya ce za a gudanar da zaben shugaban kasa, da na 'yan majalissar dattijai a dukkanin kananan hukumomin jihar 27 kamar yadda aka tsara.

Ya ce tuni hukumar ta kammala shiri domin gudanar sauran zabukan kamar yadda doka ta tanada.

Ba a dai sanar da sabuwar ranar gudanar zaben 'yan majalissar wakilan ba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China