in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun sojin Najeriya sun kwato garin Gwoza gabanin babban zaben kasar
2015-03-28 15:08:55 cri
Dakarun sojin Najeriya sun samu nasarar kwace garin Gwoza dake jihar Borno a Arewa maso Gabashin kasar daga ikon mayakan Boko Haram.

Hakan a cewar kakakin ma'aikatar tsaron kasar Chris Olukolade, ya biyo bayan hare-hare ta kasa da sama da sojojin suka kaddamar a ranar Juma'a.

Rahotanni daga rundunar tsaron kasar na cewa yanzu haka, garuruwan Abadam dake Arewacin jihar Borno, da Kala Balge, dake yankin tsakiyar jihar ne kadai suka rage a hannun mayakan kungiyar.

Wannan dai ci gaba na zuwa ne 'yan sa'o'i kadan, gabanin fara kada kuri'u a babban zaben kasar na Asabar din nan.

Tun dai a ranar Larabar da ta gabata ne shugaban tarayyar Najeriyar Goodluck Jonathan, ya yi hasashen cewa nan da ranar Juma'a sojojin kasar za su kwato garin na Gwoza.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China