in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta jaddada mahimmancin aiki da MDD a bangaren samar da zaman lafiya da tsaro
2015-02-13 15:55:17 cri

Kungiyar tarrayyar kasashen Afrika AU ta jaddada mahimmanci dake akwai na kara inganta huldar aiki tare da MDD domin zaburar da zaman lafiya da tsaro.

Shugabar kungiyar tarayyar Afrika Nkosazana Dlamini Zuma ita ce ta yi wannan kiran a yayin da ta ziyarci Addis Ababa, babban birnin Ethiopia domin halartar wata tattaunawa tsakanin kungiyar ta AU da wata tawagar MDD da kuma wasu masu fada a ji daga Afrika.

A yayin da suke musayar ra'ayi, Nkosazana ta ce, ana yin amfani da sharuddan kwamitin tsaro na MDD a dukanin ayyukan samar da zaman lafiya na Afrika domin samar da zaman lafiya a duniya.

Ta jaddada mahimmancin dake akwai na kara dankon hulda tsakanin AU da MDD domin taimakawa wajen tunkarar matsaloli masu tasowa da kuma samar da hanyoyi na karfafa hulda tsakanin bangarorin biyu. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China