in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi alkawarin tallafawa Nigeria domin murkushe Boko Haram
2015-02-11 10:51:28 cri

Magatakardan MDD Ban Ki-moon ya yi alkawarin taimakawa Nigeria tunkarar hare hare na kungiyar Boko Haram da zimmar samun nasara a kan kungiyar.

Magatakardan MDD ya gabatar da wannan tabbaci ga Nigeria a cikin wani sako wanda wakilin shi na musamman a Afrika ta yamma Mohammed Ibn Chambas ya bayyana a lokacin da ya kai ziyara ga shugaban kasar Nigeria Goodluck Jonathan a babban birnin kasar Abuja.

Magatakardan MDD ya kara da cewa, MDD ta baiwa Jonathan tabbacin cewar, za ta mara mashi baya a inda za'a maida hukumar kasa da kasa ta tabkin Chadi ta zamanto matattarar sojojin hadin gwiwa wadanda a yanzu ake kokarin hadawa domin yakar kungiyar Boko Haram.

Ban Ki-moon ya ce, MDD a karkashin bangaren samar da zaman lafiya za ta tabbatar da cewar, rundunar kiyaye zaman lafiyar ta Nigeria tana da cikakkken tsarin tafiyar da ayyukanta na tabbatar da cewar, ta murkushe kungiyar ta Boko Haram.

Magatakardan MDD ya ce, MDD za ta yi aiki tare da hukumomin Nigeria domin samar da taimakon agaji ga jama'ar da suka rasa muhallansu a jihohin da tashin hankalin ya shafa. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China