in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na son yin kokarin taimakawa Afirka cimma burin shimfida hanyoyin dogo masu saurin tafiya
2015-01-11 17:14:17 cri

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwararsa ta kasar Kenya madam Amina Mohamed sun gana da manema labaru bayan da suka yi shawarwari a tsakaninsu a birnin Nairobi, hedkwatar Kenya a ranar 10 ga wata.

Dangane da batun zuba jari kan shimfida hanyar dogo tsakanin Mombasa da Nairobi da kuma taimakawa shimfida hanyoyin dogo masu saurin tafiya a nahiyar Afirka, mista Wang ya ce, kasar Sin na son biyan bukatar Kenya ta raya ayyukan more zaman rayuwar jama'a. Haka kuma shimfida hanyar dogo a tsakanin Mombasa da Nairobi, mataki ne na farko wajen aiwatar da ra'ayi daya tsakanin shugabannin Sin da na Afirka kan shimfida hanyoyin dogo masu saurin tafiya a duk fadin nahiyar. Kasar Sin na son yin kokari wajen taimakawa kasashen Afirka cimma burinsu na shimfida hanyoyin dogo masu saurin tafiya a tsakaninsu. Mista Wang ya ce, ya yi imani da cewa, Sin da Afirka za su yi kokari tare wajen farfado da nahiyar Afirka ta hanyoyin dogo masu saurin tafiya, a karshe dai mutanen Afirka za su cimma burinsu. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China