in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta hada kai da Afirka don yaki da fataucin namun daji ba bisa doka ba
2014-01-18 16:33:41 cri
Gwamnatin kasar Sin ta bayyana kudurinta na goyon bayan kamfel din da ake a duniya na yaki da fataucin namun daji ba bisa doka ba tare da hada kai da kasashen Afirka don yaki da munanan ayyukan da suka shafi namun daji.

Darektan tabbatar da amfani da doka da samar da horo na ofishin kare namun dajin da ke fuskantar barazanar karewa a duniya na sashin kula da gandun daji na majalisar gudanarwar kasar Sin Wan Ziming ne ya bayyana hakan, yayin zaman samun horo game da yadda za a kare fataucin namun daji ba bisa doka ba a Nairobi, babban birnin kasar Kenya.

Ya ce kasar Sin, mamba ce ta kasashen da suka sanya hannun ka yarjejeniyar kasa da kasa da ta haramta fataucin namun daji ba bisa ka'ida ba. Don haka, gwamnatin kasar Sin tana goyon bayan kamfel din da ake yi na haramta farautar giwaye da karkanda a Afirka.

Darektan ya kara da cewa, suma ofisoshin jakadancin kasar Sin da kamfanoninta da ke gudanar da ayyukansu a Afirka, za su shiga a dama da su a kemfel din da ake yi.

Kwararru kan kare namun daji, sun lura da cewa, kasar Sin tana da tasiri sosai Afirka, kuma za ya iya samar da tallafin kudi da kwarewa a kokarin da ake yi na yaki da farautar namun dajin. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China