in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Congo ya yi kiran da a karfafa hadin gwiwa domin yaki da ta'addanci
2015-01-07 10:28:07 cri

Shugaban kasar Congo Denis Sassou Nguesso ya yi kira a ranar Litinin ga gamayyar kasa da kasa da ta karfafa hadin gwiwa wajen yaki da ta'addanci dake kawo barazana sosai ga zaman lafiya da tsaro a duniya. Shugaba Sassou Nguesso ya yi wannan kira a yayin bikin gabatar da sakon taya murnar sabuwar shekarar 2015 tare da jami'an diplomasiyya da kananan jakadun kasashen waje dake kasar.

Karuwar ta'addanci na kasancewa wata babbar barazana kai tsaye ga zaman lafiya, tsaron jama'a baki daya. Munanan ayyuka da tashe tashen hankalin da kungiyoyin ta'addanci ke aikata a ko'ina cikin duniya suna karya lagon kasashenmu da kuma gurgunta kokarinmu na neman ci gaba, in ji shugaban kasar Congo. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China