in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hare-hare uku a jere sun kashe jami'an tsaro 9 a garin Ouallam na Nijar
2014-10-31 10:09:10 cri

Wasu hare-haren ta'addanci da aka kai a ranar Alhamis da safe a cikin jihar Ouallam dake yankin Tillabery, a yammacin kasar Nijar, sun yi sanadiyar mutuwar mutune tara daga cikin jami'an tsaron kasar na (FDS). An kai wadannan hare-hare a jere da misalin karfe biyar na safe, kan gidan yarin birnin Ouallam, sansanin 'yan gudun hijirar kasar Mali na Manguaize da kuma kan wani ayarin sojojin yankin Tillabery dake sintiri, a cewar wata sanarwar ministan cikin gidan Nijar. Kakakin jami'an tsaro na FDS, kanal Laudru Mustapha ya bayyana cewa, adadin wucin gadin na wadannan hare-hare ya tashi zuwa mutane tara, daga cikinsu, akwai 'yan sanda biyar, jandarma biyu da garda sarki biyu, tare da jikkata wasu mutane hudu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China