Ranar 24 ga wata ne, aka yi babban zabe karo na 11 a kasar Botswana dake kudancin nahiyar Afirka tun bayan da kasar ta samu 'yancin kanta. Tawagar sa ido ta kungiya tarayyar Afirka wato AU na ganin cewa, an jefa kuri'a yadda ya kamata.
A ranar 24 ga wata da dare ne aka kammala kada kuri'ar, daga baya an fara kidayar kuri'u a wurare daban daban na kasar. Ana sa ran gabatar da sakamakon zaben nan da kwana daya zuwa biyu masu zuwa. (Tasallah)