in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Karuwar tattalin arzikin Afirka za ta wuce kashi 5 cikin 100 a cikin shekaru biyu masu zuwa
2014-10-10 10:36:27 cri
Mujallar Afirka's Pulse ta bankin duniya ta yi hasashen cewa, karuwar tattalin arzikin nahiyar Afirka za ta kai kashi 5.2 cikin 100 daga shekarar 2015 zuwa 2016.

Babban masani a fannin tattalin arziki na bankin duniya Francisco yana ganin cewa, ya zuwa yanzu nahiyar Afirka ta kasance daya daga cikin manyan yankuna uku da suka fi samu saurin bunkasuwar tattalin arziki a duniya, kana za ta ci gaba da samun saurin ci gaban tattalin arziki a cikin shekaru 20 masu zuwa. Amma, a waje guda kamata ya yi kasashen Afirka su yi share fage sosai domin tinkarar matsalolin da suka shafi karuwar gibin kudi, tabarbarewar tattalin arziki sakamakon ta'addanci, da kuma yaduwar cutar Ebola, da dai sauransu.

A cikin kasashen Afirka, a matsayinta na kasa ta biyu da ta fi samun saurin bunkasuwar tattalin arziki a nahiyar, saurin karuwar tattalin arzikin kasar Afirka ta Kudu ya ragu sosai, wanda ya kai kashi 1 cikin 100 kacal a tsakanin watan Aflilu zuwa Yuni a shekarar 2014. A nata bangaren, kasar Najeriya wadda ta kasance kasa ta farko wajen saurin bunkasuwar tattalin arziki a nahiyar, karuwar tattalin arzikinta ta kai kashi 6.5 cikin 100. Game da sauran kasashe masu karamin karfi, ciki har da Kwadibuwa, Habasha, Mozambique, Tanzaniya da dai sauransu sun tabbatar da saurin ci gaban tattalin arziki a maimakon farfadowar. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China