in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na Sin mai kula da harkokin gabas ta tsakiya ya bayyana ra'ayin Sin na yaki da ta'addanci
2014-09-26 14:57:23 cri
Manzon musamman na kasar Sin mai kula da harkokin gabas ta tsakiya Gong Xiaosheng ya bayyana wa 'yan jarida a nan birnin Beijing a yammacin ranar Alhamis 25 ga wata, inda ya ce, a cikin jawabin da ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya yi a gun taron koli na kwamitin sulhu na MDD kan yaki da ta'addanci, ya bayyana matsayin da Sin ke dauka, da kuma sabbin ra'ayoyinta kan wannan batu.

Gong Xiaosheng ya ce, Mr Wang Yi ya bayyana ra'ayin kasar Sin na sa himma wajen shiga ayyukan hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa kan yaki da ta'addanci, kana ya sanar da matsayin da Sin ke dauka kan wannan batu, wato tilas ne a bi dokokin duniya da ka'idojin dangantakar dake tsakanin kasa da kasa yayin da ake yaki da ta'addanci. Haka kuma bin kundin tsarin mulkin MDD da kudurin kwamitin sulhu yayin da ake daukar matakai, wannan matsayin da ya dace da ra'ayoyin kasa da kasa kan batun.

Daga nan sai, Gong Xiaosheng ya jaddada cewa, yanzu kasa da kasa sun dora muhimmanci sosai kan tinkarar barazanar ta'addanci, yana fatan za su iya aiwatar da hakikan ayyuka. A nata bangaren kasar Sin za ta ci gaba da daukar matakan da suka dace da kuma shiga hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa kan yaki da ta'addanci. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China