0919Murtala.m4a
|
Ranar Alhamis 18 ga wata ne, aka yi wani kasaitaccen biki na cika shekara daya cif da kafa cibiyar al'adun kasar Sin a Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya, inda kuma aka gudanar da gasar magana da harshen Sinanci a wurin. Wakilinmu Murtala dauke da karin bayani.
An dai kafa cibiyar al'adun kasar Sin wato China Cultural Centre a Abuja ne a ranar 18 ga watan Satumbar shekara ta 2013. Yanzu shekara guda ke nan da kafa wannan cibiya, inda aka shirya kasaitaccen biki don murnar wannan rana.