Sakataren harkokin waje na kasar Amurka John Kerry da babbar jami'ar EU mai kula da harkokin diplomasiyya da tsaro Catherine Ashton sun ba da wata hadaddiyar sanarwa a ran 7 ga wata cewa, suna nuna damuwa sosai kan halin kaka-ni-ka-yi da Masar ke ciki. Kuma sun sa kaimi ga bangarori daban-daban na Masar da su taimaka ga yin shawarwari tsakaninsu don ciyar da yunkurin samun sauyi gaba.
Ban da haka, shugaban kasar Amurka Barack Obama da firaministan kasar Turkiya Tayyip Erdoğan sun yi hira ta wayar tarho a wannan rana, inda suka nuna goyon baya ga Masar da ta kawo sauyi cikin dimokuradiyya. (Amina)