in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar aikin ba da agaji ta MDD za ta kai ziyarar aiki a Iraki
2014-09-11 11:05:03 cri

Mataimakiyar sakatare janar na MDD kan harkokin jin kai, Valerie Amos, za ta kai wani rangadin aiki a kasar Iraki daga ranar 11 zuwa 14 ga watan Satumba domin kimanta yadda cibiyoyin ba da agaji na MDD za su iyar tallafawa hukumomin kasar Iraki wajen kai dauki ga mutanen dake cikin bukata.

A yayin ziyararta, madam Amos za ta gana da manyan jami'an kasar Iraki da na yankin Kurdawa. Haka kuma za ta kai ziyara a wani sansanin 'yan gudun hijira, in ji cibiyar dake kula da harkokin jin kai ta MDD (OCHA) a cikin wata sanarwar da aka fitar a ranar Laraba.

Kusan 'yan kasar Iraki miliyan 1,8 suka kaura daga muhallinsu tun farkon wannan shakara, kuma tare da yanayin sanyi dake kusantowa, cibiyoyin ba da agaji da abokan aikinsu na Iraki za su cigaba da karfafa ayyukansu, in ji cibiyar OCHA. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China