A cewar wata sanarwar da ta fito daga ofishin watsa labarai na fadar shugaban kasa, mista Nkurunzizia zai gana da manyan shugabannin kasar Sin, shugabannin kamfanonin Sin da kuma daliban Burundi dake karutu a kasar Sin.
Haka kuma, shugaba Nkurunzizia zai je Nanjing, birnin dake gabashin kasar Sin, inda zai ziyarci wata makarantar wasannin motsa jiki ta Nanjing. (Maman Ada)