in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hari kan wani sansanin soja dake babban birnin kasar Congo Kinshasa
2014-07-23 10:07:17 cri
Wasu dakaru sun kai hari kan wani sansanin soja dake babban birnin kasar Congo Kinshasa a ranar 22 ga wata da yamma, amma sojan sun cimma nasarar fatattakar dakarun.

Kakakin gwamnatin kasar ya bayyana cewa, wasu dakaru sun yi yunkurin kwace wannan sansanin soja a wannan rana. Kuma wani jami'in tsaro na kasar ya ce, bangaren sojan kasar ya kama masu kai harin fiye da 20.

Gwamnatin kasar Congo Kinshasa ba ta bayyana ko akwai wadanda suka mutu ko suka raunata a sakamakon harin ba. Bisa labarin da wanda ya gane wa idonsa ya bayar, ya ce, masu kai harin guda 7 da ma'aikatan tsaron kasar biyu sun rasa rayukansu a sakamakon rikicin da ya biyo bayan harin.

Wannan lamari ya haifar da zaman zullumi a birnin Kinshasa, amma al'umma sun daidaita a wannan rana da maraice. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China