in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi allahwadai da harin da aka kai a Sudan ta Kudu
2014-07-23 09:51:46 cri

Shugabar hukumar zartaswar kungiyar tarayyar kasashen Afirka (AU) Madam Nkosazana Dlamini Zuma ta yi allahwadai da harin da aka kai a jihar Upper Nile da ke Sudan ta Kudu.

Shugabar wadda ta bayyana hakan ranar Talata cikin wata sanarwa, ta bayyana harin na ranar Lahadi da dakarun 'yan tawaye suka kaddamar a matsayin mayar da hannun agogo baya a kokarin da kasashen duniya ke yi na maido zaman lafiya a kasar.

Don haka ta yi kira ga dukkan sassan da abin ya shafa da su martaba yarjejeniyar da aka sanya wa hannu, kana su koma kan teburin sulhu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China