in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya na son amfani da makamashin hasken rana domin samar da wutar lantarki a karkara
2014-07-17 10:08:53 cri

Kasar Najeriya ta kammala wasu tsare-tsarenta na amfani da makamashin hasken rana a cikin manyan ayyukan bunkasa hanyoyin wutar lantarki zuwa yankunan karkara, in ji ministan makamashin Najeriya, Chinedu Nebo. Wannan kasa dake yammacin Afrika na aiki tare da masu ruwa da tsaki a wannan fanni domin cimma wannan buri, in ji mista Nebo a yayin wata ziyarar baki na kwalejin tsaro ta kasar Botswana a Abuja, babban birnin kasar.

Haka zalika, ministan ya jaddada cewa, ma'aikatarsa za ta bincike wasu hanyoyi da sanya ido, ta yadda masu amfani da wutar lantarki a wadannan yankuna da shirin ya shafa, da su rika biyan kudaden kulawa da kayyayakin samar da wutar lantarki ta hasken rana. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China