in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zambiya ta ce, a shirye take wajen fuskantar Ebola tare da karyata kalaman WHO
2014-07-16 10:15:31 cri

Wani babban jami'in gwamnatin kasar Zambiya ya mai da martani ga kalaman da wani jami'in kungiyar kiwon lafiya ta duniya WHO ya fitar dake cewa, kasar Zambiya ba ta shirya ba wajen yaki da cutar Ebola, in ji kamfanin dillancin labarai na Zambia Daily Mail.

A ranar Litinin, darektan WHO dake kula da rigakafin da sa ido kan cututtuka a cibiyar shiyyar Afrika, mista Francis Kasolo ya bayyana cewa, Zimbiya ba ta shirya ba wajen fuskantar Ebola dake afkawa kasashen dake gabashin Afrika.

Sai dai ministan kiwon lafiya na kasar, Joseph Kasonde ya bayyana cewa, wannan sanarwa ba ta da tushe da sabanin kalaman WHO, ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar ta aiwatar da wasu matakan da suka dace domin killace da hana yaduwar wannan cuta mai kashewa.

A cewar mista Kasonde, ma'iakatarsa ta kafa wani rukunin kwararru da ya kaddamar da kamfen horar da fadakar a cikin manyan hanyoyin shigowa cikin kasar, har ma cikin manyan filayen jiragen sama hudu na kasar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China