Yan sanda a birnin na Sao Paulo na kasar Brazil sun tarwatsa gungun masu zanga-zanga, 'yan sa'o'i kafin bude gasar cin kofin duniya ta bana. Su dai masu zanga-zangar na zargin mahukuntan kasar da kashe makudan kudade domin karbar bakuncin wannan gasa, yayin da a cewar su, manyan ababen more rayuwar jama'a, kamar fannin ilimi, da lafiya da harkar sufuri ke cikin wani mummunan yanayi a kasar. (Saminu)