in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu ta yi maraba da matsayin Najeirya na kasa mafi karfin tattalin arziki a Afrika
2014-04-08 11:02:39 cri

Kasar Afrika ta Kudu ta yi maraba da sanarwar daga matsayin Najeriya, kasa mafi yawan al'umma a nahiyar Afrika, a sahun gaba ta fuskar karfin tattalin arziki a shiyyar kasashen dake kudu da hamadar Sahara, in ji bitalmanin kasar Afrika ta Kudu a ranar Talata.

Sanarwar tana amsa sakon yau da kullum na Afrika ta Kudu tun a shekarar 1994 na cewa, muna fatan ganin karin tattalin arzikin Afrika na karuwa da kuma amfanawa arzikinsu, in ji bitalmanin kasar a cikin wata sanarwa.

Najeriya ta zama kasa mafi karfin tattalin arziki a Afrika tun lokacin da kasar ta sake duba tsarin bayananta na GDP, yawan kudin da aka samu daga sarrafa dukiyar kasa. Wato a da, ba a bayyana yawan kudin da aka samu wajen bangarorin sadarwa, fasahohin zamani, kide-kide, sayarwa ta hanyar internet, kamfanonin jiragen sama da bunkasuwar sana'ar shirya fina finai a kasar ba.

GDP din wannan kasa dake yammacin Afrika a shekarar 2013 ya kai Naira triliyan 80,3, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 509,9 idan aka kwatanta da dalar Amurka biliyan 370,3 a karshen shekarar 2013 na kasar Afrika ta Kudu, a cewar hukumar kididdiga ta Najeriya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China