in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Netherlands sun amince da kafa managarcin tsarin hadin gwiwa
2014-03-23 20:34:21 cri
Shugaba Xi jinping na kasar Sin, da firaministan kasar Netherlands Mark Rutte, sun cimma matsayar kafa wani managarcin tsarin hadin gwiwa, wanda zai daukaka huldar diplomasiyyar kasashen biyu zuwa sabon matsayi.

Shuwagabannin sun cimma wannan kuduri ne yayin ganawar da suka yi a yau Lahadi, a ci gaba da ziyarar aiki da shugaba Xi ke yi a kasar ta Netherlands.

Wata sanarwar hadin gwiwa da shuwagabannin biyu suka fitar ta ce ana fatan daukar wannan mataki, zai ba da damar gudanar da budaddiyar hadin gwiwa tsakanin sassan bBiyu, a ci gaba da fadada dangantakar Sin, da mahukuntan take kokarin yi da ragowar kasashen Turai. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China