in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar sa ido ta AL ta amince da yanayin da ake ciki gabanin babban zaben kasar Algeria
2014-03-16 17:10:24 cri
Mataimakin babban sakataren kungiyar tarayyar kasashen Larabawa (AL), Mohammed Sobeih, ya bayyana cewa kungiyar ta AL, na mai da hankali kan babban zaben da za a gudanar a kasar Algeria, tare da gamsuwa kan yanayin da ake ciki yanzu haka a kasar.

Mohammed Sobeih ya bayyana hakan ne a jiya Asabar 15 ga wata, bayan kammala shawarwari da ministan harkokin wajen Algeria Ramtane Lamamra. Inda ya ce kamata ya yi babban zaben dake tafe, ya haifar da sakamako mai kyau.

Tawagar sa ido ta kungiyar AL, dake karkashin jagorancin mista Sobeih ta isa Algeria a ranar 12 ga wata, inda ta yi shawarwari da hukumomin gwamnatin kasar, da sauran masu ruwa da tsaki.

Za dai a gudanar da babban zaben kasar ta Algeria ne a ranar 17 ga watan Afrilu mai zuwa, inda 'yan takara 6 za su shiga zaben, ciki har da shugaban kasar Abdelaziz Boutefilika.

An labarta cewa, cikin kungiyoyin da zasu tura jami'an sa ido don ganin yadda zaben zai gudana, hadda MDD, da kungiyar AL, da kungiyar tarayyar kasashen Afirka. Sauran sun hada da kungiyar tarayyar kasashen Turai, da kungiyar hadin gwiwar kasashen Musulmi da sauransu. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China