in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan lambobin kere-kere na kasar Sin dake neman iznin mallaka ya kai matsayi na uku a duniya a shekarar 2013
2014-03-14 15:47:56 cri

Kungiyar ikon mallakar fasaha ta duniya WIPO ta ba da rahoto a ran 13 ga wata cewa, adadin lambobin kere-kere na kasa da kasa dake neman iznin mallaka ya kai fiye da dubu 200 a shekarar 2013, inda Sin ta maye gurbin kasar Jamus inda ta zama a matsayi na uku, daga cikinsu, kamfanin samar da kayayyakin lantarki na ETZ da kamfnain Huawei suna sahun gaba a duniya.

Kungiyar WIPO ta bayyana cewa, a cikin shekara da ta gabata, saurin karuwar adadin da Sin ta gabatar ya kai sahun gaba a cikin kasashe goma mafi rinjaye a wannan fanni a duniya.

Babban jami'in WIPO Francis Gurry ya bayyana cewa, Sin ta gabatar da dokar ikon mallaka fassaha nan da shekaru 30 da suka gabata, ya zuwa yanzu, yawan adadin lambobin kere-kere dake neman iznin mallaka ya haura na kasar Jamus, abin da ya nuna kwarewar kasar Sin sosai a wannan fanni. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China