in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan makamashi na kasar Ghana na ziyara a kasar Sin
2014-02-18 09:39:52 cri

Mnistan makamashi da man fetur na kasar Ghana Emmanuel Armah-Kofi, yana ziyarar aiki a kasar Sin, da nufin kara janyo masu zuba jari a bangaren makamashin kasar.

Yayin ziyarar ministan a nan kasar Sin, ana sa ran zai ziyarci wasu cibiyoyin makamashi, inda zai gana tare da yin musayar ra'ayoyi da wasu manyan masu ruwa da tsaki a bangaren na makamashi a kasar ta Sin, wadanda suka hada da manyan kamfanonin samar da wutar lantarki da ke Shanghai da kuma Shenzhen, wato iyayen gidan kamfanin samar da wutar lantarki na Suno-Asogli da ke Ghana.

Wata sanarwar da ma'aikatar makamashi da man fetur ta kasar Ghana ta bayar a ranar Litinin na nuna cewa, ministan zai tattauna da jami'an wadannan kamfanonin biyu da nufin zakulo hanyoyin fadada kamfanonin samar da wutar lantarkin da ke Ghana. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China