Duk da cewa, an fara kidaya kuri'u, amma ba za a samu sakamakon zaben a ranar Lahadi ba, sai bayan an gabatar wa hukumar zaben kasar da sakamakon zaben tare da kammala zabuka a wuraren da tun farko aka hana gudanar da zaben a wasu tashoshin zaben kasar.
Rahotanni daga kafofi watsa labaran kasar na cewa, kimanin mutane miliyan 12 cikin mutane miliyan 48.77 da suka cancanci yin zabe a kasar, ba su fito zaben na ranar Lahadi ba, sakamakon toshe tashoshin zabensu da masu adawa da gwamnati suka yi da kuma wasu mazabu 28 da ba su tsayar da 'yan takara a babban zaben kasar ba.
An tsayar da ranar 23 ga watan Fabrairu a matsayin ranar zaben cike gurbi. (Ibrahim)