in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya ta bullo da sabbin matakan inganta tsaro
2013-12-10 10:22:18 cri

Shugaba Uhuru Kenyatta na kasar Kenya, ya kara fadada ayyukan sojojin kasar na murkushe barazanar tsaro a kasar da ke gabashin Afirka.

Ma'aikatar tsaron kasar ce ta sanar da hakan cikin wata sanarwa da ta bayar, inda ta bayyana cewa, shugaba Kenyatta ya bullo da wata sabuwar runduna a karkashin rundunar tsaron kasar ta Kenya (KDF), wadda za ta rika sa-ido kan batutuwan da suka shafi fataucin miyagun kwayoyi, barazanar da ake fuskanta daga 'yan ta'adda, da yaduwar kananan makamai.

Sanarwar ta ce, an kafa sabuwar rundunar ce, sakamakon barazanar da kasar ke fuskanta sakamakon wanzuwar ayyukan ta'addanci, fataucin miyagun kwayoyi, yaduwar kananan makamai, aikata manyan laifuffuka da sauran su wadanda ke kara yaduwa a birane, kamar Nairobi, babban birnin kasar.

Gwamnatin kasar Kenya, ta shirya daukar matakan ne bayan aukuwar harin ta'addancin ranar 21 ga watan Satumba da ya faru a Nairobi, inda 'yan sanda suka bullo da yin snitiri a hanyoyin shigowa kasar domin magance matsalar tsaro.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China