in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya nemi taimakon Isra'ila a fagen yaki da ta'addanci
2013-10-29 15:30:56 cri

Shugaban tarayyar Najeriya Dr. Goodluck Ebele Jonathan, wanda a yanzu haka yake ziyara a kasar Isra'ila, ya nemi taimako da hadin-kan gwamnatin Isra'ila ta fuskar murkushe ayyukan ta'addanci, wadanda ke addabar kasashen biyu a halin yanzu.

Shugaba Goodluck Jonathan yayi wannan furuci ne yayin da yake ganawa da shugaban kasar ta Isra'ila Shimon Peres a jiya Litinin a birnin Kudus, a ci gaba da aikin ibada irin ta addinin Kirista da yake gudanarwa a kasar.

Jonathan yace, Najeriya na maraba da ganin ingantar hadin-gwiwa da tallafawa juna da Isra'ila, musamman ma a fannin kawo karshen hare-haren ta'addanci, wadanda ke ciwa jama'a tuwo a kwarya a wasu sassan Najeriya.

'ina neman taimakonku da hadin-kan kasar Isra'ila, wajen dakile tabarbarewar yanayin tsaron da muke ciki, babu tantama Isra'ila tana da kwarewa sosai tsawon shekaru, a wannan fage na yaki da 'yan ta'adda, don haka Najeriya zata iya amfana daga wannan kwarewa.' A cewar shugaba Goodluck Jonathan.

Har wa yau kuma, Jonathan ya jinjinawa irin bunkasar alakar tattalin arziki, da kasuwanci tsakanin Najeriya da Isra'ila, ya kuma yi kira da a fadada hadin-gwiwa a ragowar sauran fannoni.

Murtala, wakilin sashin Hausa na CRI, daga Abuja, Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China