in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata Sin da Rasha su samu bunkasuwa tare
2013-10-22 20:14:32 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan kasar Rasha Dmitry Medvedev a yau Talata 22 ga wata a nan birnin Beijing, inda Xi ya nuna yabo ga dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa dake tsakanin Sin da Rasha, kana ya jaddada cewa, kamata ya yi kasashen biyu su kara yin hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni da kuma samun bunkasuwa tare.

Shugaba Xi ya bayyana cewa, ya kamata kasashen biyu su fahimci tasirin da dangantakar dake tsakanin Sin da Rasha ta yiwa dukkan duniya, da nuna goyon baya ga juna da kuma kara yin mu'amalar fasahohin gudanar da ayyukan kasa a tsakaninsu. Kana kasashen biyu su kara aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma daidaito bisa bukatun raya dangantakarsu a sabon halin da ake ciki don inganta hadin gwiwarsu.

A nasa bangare, Medvedev ya bayyana cewa, kasar Rasha tana son kara yin mu'amala da hadin gwiwa tare da kasar Sin a fannonin tattalin arziki, cinikayya, fasaha, makamashi da dai sauransu, da kara yin hadin gwiwa kan harkokin kasa da kasa da kuma ayyuka a karkashin tsarin hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa, ta yadda za a inganta dangantakar dake tsakaninsu zuwa wani sabon matsayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China