in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Gambia za ta yi amfani da hukuncin kisa domin magance matsalar kashe kashe da kuma ta'addanci
2012-08-20 17:05:31 cri
Shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh ya yi wani furuci a kwanan nan cewa gwamnatinsa na shirin fara aiwatar da hukuncin kisa domin kawo karshen kashe kashen mutane da kuma barazanar ta'addanci a cikin kasar.

"dukkan wasu matakan ladabtarwa da hukuntawa dake cikin dokar kasa da za su taimakawa wajen ganin duk wasu masu kawo tashin hankali cikin kasa sun dandana wukar kudarsu, kuma wadanda suka aikata kisa su ma kisa zai hau kansu" in ji shugaba Jammeh.

Haka kuma ya kara da cewa gwamnatinsa ba za ta ba da dama ga 'yan ta'adda ko masu fashi da makami su ci gaba da addabar kashi 99 cikin 100 na al'ummar kasar ba.

Shugaba Yahya Jammeh yayi wadannan kalamai a lokacin da ayyukan ta'addanci da kashe kashe, tare mutane ke kan hanya, sace sace da garkuwa da mutane suka yi kamari a cikin kasar.

"Burinmu shi ne kafa wata kasar zaman lafiya da jituwa da babu tashe tashen hankali", in ji shugaban kasar Gambia tare da daukar niyyar karfafa matakan tsaro da na shari'a domin daidaita wannan matsala. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China