in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun gwamnatin Somaliya sun lalata maboyar Al-Shabaab guda 17
2013-08-14 10:09:45 cri

Jami'ai sun baiyana ranar Talata cewa, dakarun gwamnatin kasar Somaliya sun lalata maboyar kungiyar Al-Shabaab guda 17, kana sun cafko 'yan kungiyar guda 40, a wani sumame da aka kai a Mogadishu, babban birnin kasar ta Somaliya.

Yayin da yake zantawa da 'yan jarida dangane da tabarbarewar harkokin tsaro a babban birnin kasar, ministan harkokin cikin gida da tsaron kasa Abdelkarim Hussein Guled ya baiyana cewa, wadanda ke wadannan maboya ne ke kawo rashin tsaro da tayar da hankulan 'yan kasar Somaliya.

Ya ci gaba da cewa, a kowace maboya, akwai mambobin kungiyar tsakanin 3 zuwa 11, wanda baki daya yawansu ya kai 39, kuma hukumomin tsaro na kasar suna nemansu ruwa a jallo.

Harkokin tsaro sun tabarbare a Mogadishu, babban birnin kasar a cikin 'yan makonnin nan, musamman a cikin watan Ramadan mai tsarki, wanda ya kare a makon da ya wuce. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China