in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Da wuya a kai ga mizanin karuwar cinikayyar ketare da ake son cimma, a cewar ma'aikatar cinikayyar kasar Sin
2013-06-18 18:20:54 cri
Kakakin ma'aikatar cinikayya ta kasar Sin Shen Danyang ya fada a ranar Talata cewa, kamata ya yi kasar Sin ta magance matsaloli da dama muddin tana bukatar samun kashi 8 cikin 100 na karuwar cinikayyar ketare da ake son cimmawa a shekarar 2013.

Mr Shen ya ce tafiyar hawainiyar da kasar ta fuskanta a bangaren cinikayyar ketare a watan Mayu, ya faru ne sakamakon dokokin da gwamnati ta bullo da su da nufin rage kudaden da ke kewaya a kasuwa da ake fakewa da sunan biyan kudaden cinikayya.

Ya ce karuwar darajar kudin kasar na Yuan da raguwar bukatun kayayyaki daga ketare, sun yi tasiri kan kayayyakin da ake fitarwa zuwa ketare, don haka ana ganin cewa, karuwar cinikayyar ketaren kasar a wannan shekara ba za ta yi wani tsanani ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China