Game da inda Gadhafi yake, har yanzu bangarori daban daban ba su da tabbataccen labarin maboyarsa. Wata tashar Intanet ta ruwaito jawabin da Gadhafi ya yi ta wani gidan rediyo a ran 27 ga wata bisa agogon wurin, cewar zai ci gaba da yaki a kasar Libya a maimakon gudu zuwa wani kasa. Gadhafi ya ce, zai sadaukar da kansa ne kamar wani jarumi. A 'yan kwanaki masu zuwa kuma, mahukuntan kasar Libya zasu hadu da babbar matsala da zai wuce zatonsu. Bugu da kari kuma, a cikin jawabinsa, Gadhafi ya yi suka da babbar murya ga hare-haren da kungiyar NATO ta kai ga kasar Libya. Ya mai cewa,Shugabannin kasashen yammacin duniya sun yi haka ne don kwace man fetur da kasar Libya ke da shi.