in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sin za ta kara hadin gwiwa tsakaninta da kasashen Afirka a fannin rage abkuwar bala'in fari
2011-09-26 13:52:29 cri

A yayin taron, ministan harkokin jama'ar kasar Sin Li Liguo ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin ta riga ta samar da taimakon abinci cikin gaggawa ga kasashen Afirka dake fama da bala'in ta hanyoyi daban daban. Ya ce,  "Yanzu, wasu kasashen Afirka suna fama da bala'in fari mai tsanani da karancin abinci mai tsanani, a sanadin haka, gwamnatin kasar Sin ta tsai da cewa, za ta samar da taimakon abinci mai darajar kudin Renminbi yuan miliyan 533 da dubu 200 domin taimakawa kasashe masu fama da bala'in. Ba ma kawai gwamnatin kasar Sin ta samar da taimakon abinci ba, har ma ta gabatar da kudin musaya domin sayen abinci."

Li Liguo ya ci gaba da cewa, yanzu, gwamantin kasar Sin tana kokarin cika alkawarinta, kuma, a farkon wannan wata, an riga an fara jigilar da taimakon abinci ga kasashen Afirka dake fama da bala'in, nan gaba, za a ci gaba da gudanar da wannan aiki yadda ya kamata.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China