in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An mika kamfanin Lu'u-Lu'u na kasar Ghana ga hannun 'dan kasuwa
2011-08-24 14:33:03 cri

Gwamnatin kasar Ghana ta mika kamfanin Lu'u-Lu'un kasar wato GCD ga hannun wani sabon kamfanin zuba jari mai suna GCDGL a wani bikin da aka gudanar ranar Talata a Akwatia mai nisan kilomita 80 daga arewa maso yammacin birnin Accra, hedkwatar kasar.

Lokacin da yake jawabi a bikin mika kamfanin, mataimakin shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya ba da sanarwar cewa, an baiwa kamfanonin biyu masu zaman kansu iznin gina matatar Lu'u-Lu'u a kasar Ghana, yayin da kamfanin cinikayyar ma'adinan kasar PMMC ya fadada na'urorinsa na kawata Lu'u-Lu'u.

Wannan mataki ya dace da manufar gwamnatin kasar na tabbatar da cewa, kasar ta kara inganta bangaren ma'adinai don kara samun kima a kasuwannin duniya.

Mahama ya ce, an yanke shawarar fadada kamfanin Lu'u-Lu'un kasar ne domin a ba da dama ga sassan masu zaman kansu su shiga a dama dasu a harkar samar da Lu'u-Lu'u, hakan ya kasance manufar gwamnatin kasar na mayar da sassan masu zaman kansu a matsayin ginshikin ci gaban da zai kai ga bunkasa sauran sassan tattalin arzikin kasar.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China