in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yakin da ake yi tsakanin bangarori biyu na Libya ya kara tsananta
2011-04-18 14:54:36 cri

Hakazalika, jaridar New York Times ta kasar Amurka ta bayar da wani rahoto a ran 16 ga wata, cewar yanzu gwamnatin kasar Amurka tana kokarin neman damar korar Gaddafi daga kasar Libya, wato tana neman wata kasa wadda za ta iya karbar Gaddafi. Wani jami'in kasar Amurka ya ce, "kasashen da za a iya zaba kalilan ne." Jaridar New York Times ta kiyasta cewa, mai yiyuwa ne wata kasar Afirka za ta iya karbar Gaddafi.

Game da wannan rahoton da jaridar New York Times ta bayar, manazarta sun nuna cewa, idan wannan labari ya kasance na gaskiya, to wannan na alamta cewa, kasar Amurka tana kokarin koyon darussa daga yakin Iraki, wato tana kokarin neman kungiyoyin siyasa na kasar Libya da su canja gwamnatinsu da kansu, amma ba bisa matakin soja kawai ba. Idan an iya korar Omar Mouammer al Gaddafi daga mukaminsa ta hanyar zaman lafiya, a kalla kasar Amurka za ta iya rage yawan kudin da take kebewa aikin soja.

Amma, har yanzu malam Omar Mouammer al Gaddafi na nuna adawa da irin wannan shiri na kasar Amurka. A kwanan baya, har sau da dama ne 'ya'yansa suka bayyana cewa Gaddafi ba zai sauka daga mukaminsa ba, kuma ba zai bar kasar Libya ba. (Sanusi Chen)


1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China