in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yakin da ake yi tsakanin bangarori biyu na Libya ya kara tsananta
2011-04-18 14:54:36 cri

Haka kuma, hukumar sa ido kan hakkin bil Adam ta kasa da kasa da dakarun adawa na Libya sun zargi dakarun gwamnatin Gaddafi a ran 15 ga wata cewar dakarun Gaddafi sun yi amfani da bamabamai masu kwanso a kalla sau uku a unguwannin dake birnin, amma kakakin gwamnatin Libya Saleh Ibrahim ya musunta wannan zargi har sau da yawa a ran 16 da ran 17 ga wata. Malam Ibrahim ya ce, dakarun gwamnatin ba su da irin wadannan bamabamai masu kwanso.

Dadin dadawa, dakarun adawa ba su samu rinjaye ba a filin yaki. Ko da yake kungiyoyin adawa na Libya sun nemi kungiyar NATO da ta kara samar musu kudi da makamai, amma har yanzu ba a samu matsaya daya ba kan wadannan batutuwa a cikin kungiyar NATO. Sakamakon haka, ba a san yaya kungiyar NATO za ta iya kara tallafawa kungiyoyin adawa na Libya a nan gaba ba.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China