Ban da haka kuma, bayan da aka gudanar da babban zaben kasar Cote d'lvoire a shekarar 2010, kwamitin zabe mai zaman kansa na kasar ya sanar da cewa, Ouattara ya lashe zabe, amma kwamitin tsarin mulkin na kasar ya nuna Laurent Gbagbo ya lashe zaben. Daga bisani, Alassane Ouattara da Laurent Gbagbo sun yi rantsuwar kama aiki daya bayan daya, MDD da kungiyar AU da kungiyar EU sun amince da Ouattara a matsayin shugaban kasar Cote d'lvoire, kuma gamayyar kasa da kasa sun yi Allah wadai da abin da Gbagbo ya yi.
Manazarta suna ganin cewa, watakila bangarori za su yi shawarwari a nan gaba ba da dadewa ba, kuma za a kawo karshen yakin basasa idan aka cimma matsaya daya a shawarwarin.(Lami)