in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Laurent Gbagbo sun nemi a tsagaita bude wuta
2011-04-06 13:53:24 cri

Game da matakin da za a dauka kan Laurent Gbagbo a cikin kwanaki masu zuwa, ya zama wani batun dake jawo hankalin jama'a. A ran 5 ga wata, Mr. Alain Juppe, ministan harkokin wajen kasar Faransa ya ce, Laurent Gbagbo ya samar da sharadinsa na sauka daga iko, amma kasar Faransa da M.D.D. sun neme shi da ya sa hannu kan takardar amincewa da Alassane Ouattara ya lashe zaben shugaban kasar Kodivwa. Bugu da kari, a yayin taron da kwamitin harkokin waje na majalisar dokokin kasar Faransa ya shirya, Mr. Alain Juppe ya bayyana cewa, wani mashawarci na Laurent Gbagbo ya riga ya gana da jakadan kasar Faransa dake kasar Kodivwa domin tattauna kan sharudan saukar Laurent Gbabgo daga mukaminsa da bangarorin da abin ya shafa.

Dadin dadawa, Mr. Ramtane Lamamra, wanda ke shugabancin kwamitin shimfida zaman lafiya da tsaro na kawancen kasashen Afirka, wato AU ya ce, bayan da shugaba na wannan zagaye na kwamitin ya yi shawarwari da Laurent Gbagbo, yana ganin cewa, Laurent Gbagbo ya riga ya fara tunanin yiyuwar sauka daga mukamin shugabancin kasar Kodivwa. Haka kuma, Mr. Ramtane Lamamra ya ce, kungiyar AU ba ta son ganin an kawo wa kasar Kodivwa baraka, kuma ba ta son ganin an ci gaba da yakin basasa a kasar. Kungiyar AU tana fatan a hanzarta kwantar da hankali a kasar Kodivwa, kuma a yi kokarin kafa wani kyakkyawan tushe ga yunkurin shimfida zaman lafiya, dimokuradiyya da sulhu a kasar. (Sanusi Chen)


1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China