in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Laurent Gbagbo sun nemi a tsagaita bude wuta
2011-04-06 13:53:24 cri

A ran 5 ga wata, Mr. Hamadoun Toure, kakakin kungiyar M.D.D. dake kasar Kodivwa ya gaya wa manema labaru ta wayar tarho, cewar a wannan rana, manyan hafsoshi uku na Laurent Gbagbo sun buga waya ga kungiyar M.D.D. dake kasar Kodivwa, inda suka bayyana cewa, sun riga sun ba da umurnin tsagaita bude wuta, kuma suna tsara shirin kawo karshen yaki. Bugu da kari, wadannan manyan hafsoshi suna nuna niyyarsu ta mika makamansu ga kungiyar M.D.D. dake kasar Kodivwa baya da haka kuma sun bukaci kariya daga kungniyar. Mr. Toure ya ce, yanzu Laurent Gbagbo ya rasa mabiya. Haka kuma, a yayin wani taron manema labaru, Mr. Martin Nesirky, kakakin babban sakataren M.D.D. ya sanar da cewa, ana tattaunawa kan batun saukar Laurent Gbagbo daga mukaminsa. Bisa labarin da kungiyar M.D.D. dake kasar Kodivwa ta bayar, an ce, yanzu Laurent Gbagbo a boye yake a wani dakin da boma-bomai ba su ratsa shi dake cikin fadar shugaban kasar Kodivwa, amma dakarun Alassaine Ouattara sun riga sun kewaye shi.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China