in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sin da Botswana sun tattauna kan harkokin ciniki da tattalin arziki
2010-09-15 20:07:47 cri
Ran 26 ga wata, a nan Beijing, kasashen Sin da Botswana sun yi taron tattaunawa kan ciniki da tattalin arziki, inda suka daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa ta fuskar zuba jari da ciniki da raya manyan ayyuka da dai sauransu, sun kuma samu ra'ayi daya kan yadda za su inganta hadin gwiwa ta fagen tattalin arziki da ciniki a nan gaba.

Kasashen Sin da Botswana sun kulla dangantakar diplomasiyya a shekarar 1975. A cikin shekaru 35 da suka wuce, kasashen 2 sun raya dangantakarsu yadda ya kamata, suna ta yin mu'amala ta fagen ciniki da tattalin arziki. Ya zuwa karshen shekarar 2009, kasar Sin ta zuba dalar Amurka biliyan 735.3 a Botswana kai tsaye. Sa'an nan kuma, masana'antun kasar Sin sun taka rawa a ayyukan gine-gine a Botswana, suna ba da gudummawa sosai wajen kyautata ayyukan jin dadin jama'a da ma fasahohi a wurin.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China