in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shirya taron kara wa juna sani kan matakan samun bunkasuwa tsakanin Sin da kasashen Afrika
2010-09-15 17:14:30 cri

A ranar 14 ga wata a nan birnin Beijing, an shirya taron kara wa juna sani kan yunkurin samun bunkasuwa a karo na uku tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika a karkashin shugabancin ma'aikatar kudi da ma'aikatar kasuwanci ta kasar Sin, da ofishin samar da tallafi na majalisar gudanarwa ta kasar, da kuma bankin duniya. Babban taken taron shi ne, 'bunkasa manyan gine-gine da yankunan musamman na raya tattalin arziki da fasaha.'

A cikin jawabinsa, mataimakin ministan kudi na kasar Sin, Wang Jun ya nuna cewa, 'A cikin shekaru fiye da 30 da suka wuce bayan aiwatar da manufar yin gyare-gyare da bude kofa ga kasashen ketare, kasar Sin ta samu babbar nasara a fannoni daban daban. Wannan ya nuna cewa, a yayin da ake kokarin yin tsayin daka kan samun 'yancin kai, da aiwatar da harkoki na cin gashin kai, kamata ya yi a kara kokarin samun bunkasuwar tattalin arzikin duniya kuma ya zamo bai daya. Ya kamata a nemi wata hanyar bunkasuwa bisa yanayin da kasar ke ciki, da kuma inganta samun sakamako mai kyau a nan gaba ta hanyar yin gyare-gyare. Muna son gabatar da fasahohin da muka mallaka wajen samun bunkasuwa ga kasashe daban daban na Afrika.'

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China